Ƙungiyar IS ta ce ta ƙaddamar da wani hari ranar Juma'a kan wani shingen bincike a garin Isma'ilia da ke Masar inda wasu ƴan Sanda Uku suka mutu.
Shi ne hari irinsa na farko da aka kai a Masar cikin shekaru uku, ko da yake ana ci gaba da samun tashin hankali a yankin Sinai mai maƙwabtaka.
Ƴan Sanda sun ce sun kashe wani mahari, guda kuma ya tsere.