Get Even More Visitors To Your Blog, Upgrade To A Business Listing >>

Ambaliya ta kora mutane wurin da aka binne bama-bamai a Sudan ta Kudu


Wata mummunar ambaliyar ruwan da ba a taba ganin irinta ba a Cikin shekara fiye da 50, da ta shanye gefen Kogin Nilu a bara, ta sa dubban 'yan Sudan ta Kudu kaura zuwa wasu tsofaffin barikokin soji da ke kan tudu.

Kauyen Canal da ke jihar Jonglei ya kasance wani wurin da sojoji suka taba amfani da shi a baya, shi da birnin Malakal da ke gaba da nan, dukkaninsu suna gefen Kogin Nilu.

Sai dai sabbin mazauna wurin sun fada cikin wani tashin hankali, bayan da suka fahimci cewa akwai wani tsohon inda da aka binne bama-bamai a wurin.

Mutanen da yaki ya kore su daga gidajensu sun shiga gujewa ambaliyan ruwa da ta kusan kai wa Lamarin da ke ci gaba da zama wata babbar matsala a cikin shekara hudu da suka gabata.

An yi kiyasin cewa mutane miliyan 2.2 watau kusan kashi 20 cikin dari na al'umar sun rasa matsugunansu a cikin kasar.

Yayin da Majalisar Dinkin Duniya ke bayyana fargabar cewa, kimanin mutanen kasar miliyan 10 za su bukaci tallafin abinci a shekarar 2023. 












A wani yunkurin ganin ta tseratar da iyalinta daga ambaliyar da ta shanye kauyensu, Mary Nyantey (wadda ke cikin hoto na sama) ta daure 'ya'yanta biyar a wata ledar da ake amfani da ita wajen rufe gidaje saboda ruwan sama.

Inda ta shafe tsawon kwana guda tana iyo a cikin kogin, tana jan buhun da yaran ke ciki har ta isa garin Bentiu.

A yanzu iyalin na zaman gudun hijira a can, amma ba su da abinci sai suke zuwa kogin suna shuka wani abin da ake kira "yell", abin da suke ci kenan domin su rayu.


Sansanin 'yan gudun hijirar da ke Bentiu na dauke da mutane fiye da 112,000 kuma sansanin na sama wani tudun da aka gina don kare ambaliyan ruwa.

Jami'in hukumar kula da 'yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya, Joshua Kanyara, ya ce wurin a bushe yake saboda ginin da kungiyoyin agaji suka yi ya kai tsawon mita 2.5 (kafa 8 da inci biyu).

Gatkuoth Makal Kuir (wanda ke hoto na sama) yana da shekara 19 lokacin da ya isa sansanin 'yan gudun hijirar a shekarar 2014, bayan ya kwashe kwana hudu yana tafiya da kafa, domin tserewa dakarun gwamnati da suka ce kauyensu na boye abokan gaba.

A yanzu shekarsa 27, kuma yana son komawa gida, amma baya jin zai iya daukar nauyin matarsa da dansa idan sun koma saboda ambaliya.

Yana wuni wajen neman itace, inda yakan yi tafiya mai nisan gaske, a don haka rashin tsaro na damunsa, musamman ma saboda rahotannin da suka samu na cewa dakaru sun kwashe wasu matasa 30, inda suka tilasta musu shiga soji kuma aka kashe su a fagen daga.Nyawoura Dak Top (wadda ke hoto na sama) ta yi zaman gudun hijira a wani sansani da ke kasar Kenya,ta dawo wannan sansanin a bara domin neman mahaifiyarta.

An shaida mata cewa ta rasu a lokacin da aka fara yakin, amma lokacin da ta ji cewa mai yiwuwa tana Bentiu, sai ta zo nemanta.

Sun shiga cikin farin cikin da baya misaltuwa a lokacin da suka hadu, kuma tun daga sannan suke zaune tare.

Sai dai Nyawoura tana jinta a takure, a wannan sansanin saboda ci gaba da fuskantar ambaliyan ruwa. Tana so ta yi karatu, amma tana tsoron 'yan uwanta za su iya yi mata auren dole.




This post first appeared on Duniyar Net, please read the originial post: here

Share the post

Ambaliya ta kora mutane wurin da aka binne bama-bamai a Sudan ta Kudu

×

Subscribe to Duniyar Net

Get updates delivered right to your inbox!

Thank you for your subscription

×