Gen. TchianiJagoran juyin mulkin da aka yi Nijar ya yi Allah-wadai da takunkuman da ƙungiyar ECOWAS ta sanyawa ƙasar, yana mai bayyana su a matsayin abin da ya saɓawa doka da kuma rashin adalci.Cikin wani sako da ya gabatarwa al'ummar ƙasar ta talbijin, janar Abdoramane Tchiani, ya ce gwamnatinsa ba zata yarda ƙasashen yamma ko na yankin Afirka su matsawa ƙasarsa lamba a kan a mayar da Bazoum